Ring ring
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
**AKIDOJIN AHLUSSUNNAH Kashi na 01**

*بسم اله الرحمن الرحيم*

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا وسيات أعمالنا، من يهده الله فلا مضل له، ومن يضلل فلا هادي له وأشهد أن ﻻ إله إﻻ الله وحده ﻻ شريك له، وأشهد أن محمدا عبده ورسوله، أما بعد

Assalamu Alaikum InshaAllah zan fara rubutu dan gane da Akidar Ahlussunnah wal'jama'ah Inda InshaAllah zan Kawo su kuma da dalilan su daga Al'kitabu Was-Sunnah A bisa Fahimatar Magabata na Kwarai!,

A wannan rubutu InshaAllah zan bi salo kamar Haka:-

*Ba Tsawaita rubutu,
*Kuma ba lallai na tafi a jere Kullum ba,
*Zan Taqaitu ga Kur'an da Hadisi Kamar yanda na gaya a baya bisa Fahimatar magabata,
*InshaAllah zan kokarin kawo maraji'I na abnd na kawo,

Kafin na Kutsa zan danyi Shimfida kadan Game da Akidar mu:-

Akida ta Ahlussunnah Wal'jama'ah Itace Addini Na Gaskiya Kuma Itace Akidar da Ta wajaba dukkan musulmi ya Kudurce domin Itace Hanyar da Annabi (s.a.w) da Sahabban shi suka bi, Yazo a Hadisi Annabi (s.a.w) yace:

"وستفترق هذه الأمة علي ثلاث وسبعين فرقة، كلها في النر إﻻ واحدة، قالو من هى يا رسول الله؟ قال : "من كان علي مثل ما أنا عليه وأصحابي"

Ma'ana: Annabi (s.a.w) yace:

"Da sannu wannan Al'umma zata rarraba izuwa kashi 73 Dukkan su suna wuta sai dai guda 1 (Sai Sahabbai) Suka ce: wacce ce Ita ya Ma'aikin Allah??
Sai Annabi (s.a.w) yace:
"Wadan da suka kasance akan abinda nake da sahabbai na"

[Tirmiziy 2641, Al'bani ya Inganta shi a صحيح الجامع 5343 ],

Idan muka kalli wannan Hadisi zamu ga Annabi (s.a.w) ya Siffanta wancan kashi da masu bin sa da kuma sahabban sa ma'ana Aikin su ya zama na aikin Annabi (s.a.w) ne da sahabban sa ba sabanin Hakan ba! Don Haka ashe riqo da Sunnar Annabi (s.a.w) wajibi ne ga duk mai son ya tsira a ranar Al'kiya ma,

Yazo a wani Hadisin Annabi (s.a.w) yace:

"عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الرا شدين المهديين ، عضوا عليها با لنواجذ،"
Ma'ana:
"Na hore ku Da (yin riko) Da sunnata da Sunnar Khalifofi Shiryayyu, Kuyi riko Da Ita da Fikoki"

[Abu Dawud 4607, Tirmiziy 2676, Ibn Majah 42.]

Imamu Malik (R.H) yace:

"لن يصلح أخر هذه الأمة إﻻ بما صلح به أولها"
Ma'ana:
"(Mutanen) Karshe na wannan Al'ummah ba za su taba rabauta ba se da Abinda na Farkon ta suka Rabauta dashi"

Su waye na farkon??
Hanyar Su wa kenan??

Wannan ya kara Fassara Hadisin can na sama Don haka mu muka ce Sunnah Sak!!!!!

Kuma Ahlussunnah wadanda suka bi wannan Hanya Sune wadanda Allah Yake Taimaka A nan duniya. Kuma Itace Allah yake tseratar Da Ita a ranar Al'iyama,

Zamu tsaya anan se a rubutu na gaba,

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah),
27/04/2015,


**AKIDOJIN AHLUSSUNNAH Kashi na 02**

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا وسيات أعمالنا، من يهده الله فلا مضل له، ومن يضلل فلا هادي له وأشهد أن ﻻ إله إﻻ الله وحده ﻻ شريك له، وأشهد أن محمدا عبده ورسوله، أما بعد

Cigaba..

Assalamu Alaikum. Yau zan dora daga Inda na tsaya a baya, yana da kyau ka karanta rubutun da ya gabata In baka karanta ba domin Fahimtar Inda muka dosa, Domin Karantawa shiga wannan rubutun na kasa:

http://www.basheerjournalistsharfadi.xtgem.com/akidojin%20ahlussunnah

In ba'a manta ba a rubtuna da ya gaba ta na tsaya ne akan:

Kuma Ahlussunnah wadanda suka bi waccan Hanya Sune wadanda Allah Yake Taimaka A nan duniya. Kuma Itace Allah yake tseratar Da Ita a ranar Al'iyama,

Yazo a wani Hadisi Ananbi (s.a.w) ya fada cewa: Babu wata Tawaga da ga cikin Al'umar sa da zata hadu a bisa gaskiya (Gaskiya Itace Bin wannan Hanyar da Annabi (s.a.w) ya siffanta a hadisin da muka kawo a baya) Sai Allah ya taimake ta, kamar yadda Muslim ya rawaito a 1920, Abi Dawu da Tirmiziy da Ibn majah Da Ahmad duk sun rawaito shi,

A cikin Al'kur'ani mai Girma Allah (s.w.a) yace:

"فأيدنا الذين ءامنو علي عدوهم فأصبحوا ظهرين"
Ma'ana:
"Sai muka Karfafi wadanda sukayi Imani akan Makiyan su, saboda Haka suka wayi gari suna masu rinjaye (Cin nasara)"

[Suratu الصف aya ta 14],

A wani gun Allah (s.w.a) yace:

"وإن جندنا لهم الغلبون"
Ma'ana:
"Kuma Hakika Rundunar mu sune Marabauta"

[Surats الصافات aya ta 173],

Wannan yana nuna mana Ahlussunnah ba'a rinjayar su da Hujja ko da Makami ko da wani Abu shi yasa Allah yake taimakon Ahlussunnah a dukkan Al'amuran su, Ga Kwarjinin da suke dashi a Idon Jama'a yanzu ko a cikin Abokanan ka In suka Fahimci kai mai Gaskiya ne mai Amana se kaji sunce da kai:-

"KAI se kace Dan IZALA??"

Kuma akidar Ahlussunnah da yace babu wani Kumbiya babu kwatance-kwatance Babu Bin Secular ba haushe yace ba'a yiwa gaskiya ado!! Allah (s.w.a) yace:

"فما ذا بعد الحق إﻻ الضلل"؟
Ma'ana:
"To menene A. Bayan Gaskiya face Bata?"

[Suratu ينوس aya ta 32],

Ahlussunnah Basu sakin Maganar Annabi (s.a.w) su kama ta wani ko wanene,

Zamu tsaya anan se a rubutu na gaba,

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah),
28/04/2015,


**AKIDOJIN AHLUSSUNNAH Kashi na 03**

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا وسيات أعمالنا، من يهده الله فلا مضل له، ومن يضلل فلا هادي له وأشهد أن ﻻ إله إﻻ الله وحده ﻻ شريك له، وأشهد أن محمدا عبده ورسوله، أما بعد

Cigaba..

Assalamu Alaikum. Yau zan dora daga Inda na tsaya a baya, yana da kyau ka karanta rubutun da ya gabata In baka karanta ba domin Fahimtar Inda muka dosa, Domin Karantawa shiga wannan rubutun na kasa:

http://www.basheerjournalistsharfadi.xtgem.com/akidojin%20ahlussunnah

Su Ahlussunnah Basu da wani Suna Ko Lakabi da ake kiran su da shi Idan ba Sunnah ba, Se dai Ko Abinda ke nuni Izuwa ga Sunnar,

An tambayi Imamu Malik (R.H) akan : Suwaye Ahlussunnah ?? Sai yace:

"أهل السنة الذين ليس لهم لقب يعرفون به، ﻻ جهمي وﻻ قدري وﻻ رافضي"
Ma'ana:
"Ahlussunnah sune wadanda Basu da wani Lakabi da aka san su dashi, Ba Jahmiya Ko Kadariyya Ko rafidiyya"

[Duba كتب الإنتفاء na إبن عبد البر shafi na 35],

عبد الرحمن بن مهدي. Yace An Tambayi Imamu Malik game da Sunnah sai Yace.
"هي ماﻻ اسم له غيره السنة ، وتلي: "وأن هذا صرطي مستقيما فاتبعوه وﻻ تتبعوا السبل فتفرق بكم عن سبيله"
Ma'ana:
Imamu Malik yace: Ita Bata da wani Suna Face Sunnah' Sannan se ya karanto Fadin Allah (s.w.a) cewa:

"Kuma Hakika wannan ne Hanya ta madai-dai ci Sai Ku bi shi (hanyar ta sa), Kuma Kada Kubi wasu hanyo sai su rarrabu daku Ga barin Hanya ta"
[Sutul An'am aya ta 153],

[إمام الشاطبي ya fada a cikin الأعتصام 1/79],

Ibnul Qayyum Yake fada a cikin [ مدارج السالكين 3 /179] cewa an tambayi wani daga cikin A imma game da sunnah sai yace:

"ماﻻ إسم له سوي السنة"
Ma'ana:
"Basu da wani Suna Face sunnah"

Allahu Akbar shi yasa ba'a kiran mu da yan darikar wane... Se dai ajingina mu ga sunnar Annabi (s.a.w) Duk abinda za'a Kira mu dashi zaka ga yana komawa ne Izuwa ga Sunna, To Indai haka ne an raba kenan ku kun dauki naku muma mun dauki namu Shi ya sa idan kace dani:

AHLUSSUNNAH: Daman ni mabiyin Sunnar Annabi ne don haka kowa yana jingina kanshi da shehin sa don ya nuna wanda yake bi ni kuwa se ka jingina ni ga Lamba daya daman kuma ni shi nake bi shine nawa ganin,

In Ka Kirani da:

DAN IZALA: Se nai godewa Allah ka jingina ni ga Kungiyar dake Kauda Bidi'a Tana Tsaida Sunnah, Kungiyar dake Yada Addinin Allah Kaf Africa ynz ma duk duniya Izala ta ratsa, kuma daman ni Dan Izalar ne, Don Haka sai Hamdala,

In ka kirani:

DAN SALAFIYYA: Nan ma dai Kaya ya tsinke a gindin kaba ka siffantani da mai bin Tafakin magabata wanda mun kawo bayani a baya, Kuma dama ai tafarkin su shine abin bi,

In ka kirani:

BAWAHABIYE: Al'wahab Sunan Allah ne Kuma Ni bawan sane!

Allahu Akbar! Sunnah Hantsi Leka Gidan Kowa!!

Zan Tsaya Anan kuma nan ne karshen Yar shimfidar tawa kai tsaye kuma zan kutsa, se a rubutu na gaba,

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah),
29/04/2015,


*Koma Saman Shafi*

→Labarai

**DA GASKENE WAI BA'A SAUKAR DA QUR'ANI BA DON A HADDACE SHI?** (1)

DA GASKENE WAI BA'A SAUKAR DA QUR'ANI BA DON A HADDACE SHI?
(1)
.
Assalamu alaikum wr, Haqiqa Allah ya saukar da Al-Qur'ani mai girmane don a Haddace shi, kuma ayi Zurfin Tunani a cikinsa, amma dayake Haddace Qur'ani ba abune mai sauqi ga kasalalle Rafkananne ba, kuma ba abune mai yiwuwa ga Munafuqi ba, ya sai Aka wayi gari ana mana ALFAHARI DA JAHILCI DA KASALA! Wai Allah bai saukar da Al-Qur'aniba don A haddace shi! Subhanallah! Ba mamaki don ka fadi haka, tunda baka Haddace Qur'anin ba, ga Dalilai kan Haddace Qur'an daga Qur'ani da Hadisi:
.
1: DALILAI DAGA ALQUR'ANI: Allah yace: "Kada ka motsa harshenka dashi don kayi gaggawa dashi, lallai hadashi (a qirjinka) da karantashi na garemu * duk sanda muka karantashi to kabi karatunsa * sannan bayaninsa na garemu (zamu sanar dakai)" -Suratul Qiyaamah: 16-19-. Manzon Allah s.a.w yakasance duk sanda Wahayi ya sakko masa, yana gaggawa wajen karanta Qur'anin a sanda Jibril a.s ke karanta masa, sai Allah ya Umarceshi da ya daina Gaggawa, zai tsare Qur'anin a Qirjin Manzon Allah s.a.w, ya zama a haddace kenan! Don ka gane cewa Haddace Al-Qur'ani shine matakin Farko wajen saninsa, sai Allah ya soma kawo Haddarsa (JAM'INSA) a farko, sannan Tilaawa, sannan sai sanin Tafsirinsa (BAYAANAHU), wannan ne sirrin dayasa Allah ya jero abin daki-daki!
.
2: Allah yace: "Lallai mu muka saukar da Ambato (Alqur'ani) kuma mune masu kariya gareshi" -Hijr:9-. Haqiqa kuwa Allah ya tsare Qur'ani ne ta hanyar mahaddatansa, tun daga Zamanin sahabbai har zuwa yau, domin ba Allah ne zai sakko ba ya dinga Gadin Qur'ani, kuma ba Mala'ikune zasu tsareshi kada a tabashi ba, a'a, Mahaddata Haziqai Jaruman mazaje da Mataye sune Allah yayi Amfani dasu wajen kare Al-Qur'ani, kamar yanda Hadisi ya Tabbata gameda Rubuta Al-Qur'ani a zamanin S. Abubakar r.a! Munga rawar da Mahaddata suka taka wajen Rubuta Qur'ani!
.
3: Don ka tabbatar da Cewar Lallai Qur'ani Haddarsa ake, sai mu jaka zuwa suratul Ankabut Inda Allah ke cewa: "Baka kasance kana karanta wani littafi ba gabaninsa (Qur'ani) bakuma ka rubutashi da hannunka, Ai da sai masu barna suyi shakka * A'a (Shi Qur'ani) AAYOYINE BAIYANANNU A QIRAZAN WADANDA AKA BAWA ILIMI, kuma babu masu jayayya da Ayoyinmu face azzalumai". -Ankabur: 48-49-.
.
Ashe kenan Ma'abota ilimi na haqiqa sune ke Daukeda Aayoyin Qur'ani a Qirjinsu! Kamar yanda Allah da kansa ya fadi, Yasanya duk wani Malami a Duniya, a da ko a yau, zakuga tun yana qaramin yaro ya haddace Qur'ani, shine ginshiqi na farko a duniyar karatu! Amma shi kuwa akasin haka! Qur'ani bai zama a Qirjinsa, don Qur'ani be haduwa da akasinsa a zuciya daya.
.
Babbar Ni'imar da Allah yayiwa wannan Al-ummah tun farkonta zuwa yau itace ni'imar HADDACE QUR'ANI, in muka duba zamuga adadi mai yawa daga cikin Sahabbai sun haddace Qur'ani, har a yaqin BI'IRU MA'UWNAH mahaddata 70 ne sukai shahada, hakanan ya yaqin YAMAAMAH, mahaddata 70 ne sukai shahada!
.
Zamuga cewar Annabi s.a.w yasha tura sahabbansa garuruwa koyarda Al-qur'ani da Addini, kamar Mus'ab bn Umair, wanda ya aikashi Madina, da Abdullahi bn Ummi Makhtum, wanda shi Makaho ne ma, amma dake abin a Qirji ne, da Mu'azh bn Jabal Zuwa Makkah bayan Hijrah don karantar da Qur'ani da Addini! Kuma muga yanda a lokacin sahabbai ke rige-rigen Haddace Al-Qur'ani, da sanya Yayansu zaurukan Haddace Qur'ani, wanda a Qarshe dayawansu sun haddace Qur'ani da Qira'o'I daban daban! In muka dubi Qaramin Misali, lokacin da Sahabbai sukai Hijrah zuwa Habasha, ai Ba Qur'ani suka bude suka karantawa Najjashi ba, a'a Hadda ce!
.
Don Haka in Allah bai sanyaka cikin Jakadun Al-Qur'ani ba masu bashi kariya, to kada ka soki Mahaddatan ko haddar, koda yake masu hikima na cewa: AL-INSAANU ADUWUL-LIMA JAHILA.
.
Zamu hadu a kashi na 2!

Back to posts
This post has no comments - be the first one!

UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake United States

Adadin Maziyarta 294940

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358