Polaroid
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
**AKIDOJIN AHLUSSUNNAH Kashi na 01**

*بسم اله الرحمن الرحيم*

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا وسيات أعمالنا، من يهده الله فلا مضل له، ومن يضلل فلا هادي له وأشهد أن ﻻ إله إﻻ الله وحده ﻻ شريك له، وأشهد أن محمدا عبده ورسوله، أما بعد

Assalamu Alaikum InshaAllah zan fara rubutu dan gane da Akidar Ahlussunnah wal'jama'ah Inda InshaAllah zan Kawo su kuma da dalilan su daga Al'kitabu Was-Sunnah A bisa Fahimatar Magabata na Kwarai!,

A wannan rubutu InshaAllah zan bi salo kamar Haka:-

*Ba Tsawaita rubutu,
*Kuma ba lallai na tafi a jere Kullum ba,
*Zan Taqaitu ga Kur'an da Hadisi Kamar yanda na gaya a baya bisa Fahimatar magabata,
*InshaAllah zan kokarin kawo maraji'I na abnd na kawo,

Kafin na Kutsa zan danyi Shimfida kadan Game da Akidar mu:-

Akida ta Ahlussunnah Wal'jama'ah Itace Addini Na Gaskiya Kuma Itace Akidar da Ta wajaba dukkan musulmi ya Kudurce domin Itace Hanyar da Annabi (s.a.w) da Sahabban shi suka bi, Yazo a Hadisi Annabi (s.a.w) yace:

"وستفترق هذه الأمة علي ثلاث وسبعين فرقة، كلها في النر إﻻ واحدة، قالو من هى يا رسول الله؟ قال : "من كان علي مثل ما أنا عليه وأصحابي"

Ma'ana: Annabi (s.a.w) yace:

"Da sannu wannan Al'umma zata rarraba izuwa kashi 73 Dukkan su suna wuta sai dai guda 1 (Sai Sahabbai) Suka ce: wacce ce Ita ya Ma'aikin Allah??
Sai Annabi (s.a.w) yace:
"Wadan da suka kasance akan abinda nake da sahabbai na"

[Tirmiziy 2641, Al'bani ya Inganta shi a صحيح الجامع 5343 ],

Idan muka kalli wannan Hadisi zamu ga Annabi (s.a.w) ya Siffanta wancan kashi da masu bin sa da kuma sahabban sa ma'ana Aikin su ya zama na aikin Annabi (s.a.w) ne da sahabban sa ba sabanin Hakan ba! Don Haka ashe riqo da Sunnar Annabi (s.a.w) wajibi ne ga duk mai son ya tsira a ranar Al'kiya ma,

Yazo a wani Hadisin Annabi (s.a.w) yace:

"عليكم بسنتي وسنة الخلفاء الرا شدين المهديين ، عضوا عليها با لنواجذ،"
Ma'ana:
"Na hore ku Da (yin riko) Da sunnata da Sunnar Khalifofi Shiryayyu, Kuyi riko Da Ita da Fikoki"

[Abu Dawud 4607, Tirmiziy 2676, Ibn Majah 42.]

Imamu Malik (R.H) yace:

"لن يصلح أخر هذه الأمة إﻻ بما صلح به أولها"
Ma'ana:
"(Mutanen) Karshe na wannan Al'ummah ba za su taba rabauta ba se da Abinda na Farkon ta suka Rabauta dashi"

Su waye na farkon??
Hanyar Su wa kenan??

Wannan ya kara Fassara Hadisin can na sama Don haka mu muka ce Sunnah Sak!!!!!

Kuma Ahlussunnah wadanda suka bi wannan Hanya Sune wadanda Allah Yake Taimaka A nan duniya. Kuma Itace Allah yake tseratar Da Ita a ranar Al'iyama,

Zamu tsaya anan se a rubutu na gaba,

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah),
27/04/2015,


**AKIDOJIN AHLUSSUNNAH Kashi na 02**

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا وسيات أعمالنا، من يهده الله فلا مضل له، ومن يضلل فلا هادي له وأشهد أن ﻻ إله إﻻ الله وحده ﻻ شريك له، وأشهد أن محمدا عبده ورسوله، أما بعد

Cigaba..

Assalamu Alaikum. Yau zan dora daga Inda na tsaya a baya, yana da kyau ka karanta rubutun da ya gabata In baka karanta ba domin Fahimtar Inda muka dosa, Domin Karantawa shiga wannan rubutun na kasa:

http://www.basheerjournalistsharfadi.xtgem.com/akidojin%20ahlussunnah

In ba'a manta ba a rubtuna da ya gaba ta na tsaya ne akan:

Kuma Ahlussunnah wadanda suka bi waccan Hanya Sune wadanda Allah Yake Taimaka A nan duniya. Kuma Itace Allah yake tseratar Da Ita a ranar Al'iyama,

Yazo a wani Hadisi Ananbi (s.a.w) ya fada cewa: Babu wata Tawaga da ga cikin Al'umar sa da zata hadu a bisa gaskiya (Gaskiya Itace Bin wannan Hanyar da Annabi (s.a.w) ya siffanta a hadisin da muka kawo a baya) Sai Allah ya taimake ta, kamar yadda Muslim ya rawaito a 1920, Abi Dawu da Tirmiziy da Ibn majah Da Ahmad duk sun rawaito shi,

A cikin Al'kur'ani mai Girma Allah (s.w.a) yace:

"فأيدنا الذين ءامنو علي عدوهم فأصبحوا ظهرين"
Ma'ana:
"Sai muka Karfafi wadanda sukayi Imani akan Makiyan su, saboda Haka suka wayi gari suna masu rinjaye (Cin nasara)"

[Suratu الصف aya ta 14],

A wani gun Allah (s.w.a) yace:

"وإن جندنا لهم الغلبون"
Ma'ana:
"Kuma Hakika Rundunar mu sune Marabauta"

[Surats الصافات aya ta 173],

Wannan yana nuna mana Ahlussunnah ba'a rinjayar su da Hujja ko da Makami ko da wani Abu shi yasa Allah yake taimakon Ahlussunnah a dukkan Al'amuran su, Ga Kwarjinin da suke dashi a Idon Jama'a yanzu ko a cikin Abokanan ka In suka Fahimci kai mai Gaskiya ne mai Amana se kaji sunce da kai:-

"KAI se kace Dan IZALA??"

Kuma akidar Ahlussunnah da yace babu wani Kumbiya babu kwatance-kwatance Babu Bin Secular ba haushe yace ba'a yiwa gaskiya ado!! Allah (s.w.a) yace:

"فما ذا بعد الحق إﻻ الضلل"؟
Ma'ana:
"To menene A. Bayan Gaskiya face Bata?"

[Suratu ينوس aya ta 32],

Ahlussunnah Basu sakin Maganar Annabi (s.a.w) su kama ta wani ko wanene,

Zamu tsaya anan se a rubutu na gaba,

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah),
28/04/2015,


**AKIDOJIN AHLUSSUNNAH Kashi na 03**

إن الحمد لله نحمده ونستعينه ونستغفره ونعوذ بالله من شرور أنفسنا وسيات أعمالنا، من يهده الله فلا مضل له، ومن يضلل فلا هادي له وأشهد أن ﻻ إله إﻻ الله وحده ﻻ شريك له، وأشهد أن محمدا عبده ورسوله، أما بعد

Cigaba..

Assalamu Alaikum. Yau zan dora daga Inda na tsaya a baya, yana da kyau ka karanta rubutun da ya gabata In baka karanta ba domin Fahimtar Inda muka dosa, Domin Karantawa shiga wannan rubutun na kasa:

http://www.basheerjournalistsharfadi.xtgem.com/akidojin%20ahlussunnah

Su Ahlussunnah Basu da wani Suna Ko Lakabi da ake kiran su da shi Idan ba Sunnah ba, Se dai Ko Abinda ke nuni Izuwa ga Sunnar,

An tambayi Imamu Malik (R.H) akan : Suwaye Ahlussunnah ?? Sai yace:

"أهل السنة الذين ليس لهم لقب يعرفون به، ﻻ جهمي وﻻ قدري وﻻ رافضي"
Ma'ana:
"Ahlussunnah sune wadanda Basu da wani Lakabi da aka san su dashi, Ba Jahmiya Ko Kadariyya Ko rafidiyya"

[Duba كتب الإنتفاء na إبن عبد البر shafi na 35],

عبد الرحمن بن مهدي. Yace An Tambayi Imamu Malik game da Sunnah sai Yace.
"هي ماﻻ اسم له غيره السنة ، وتلي: "وأن هذا صرطي مستقيما فاتبعوه وﻻ تتبعوا السبل فتفرق بكم عن سبيله"
Ma'ana:
Imamu Malik yace: Ita Bata da wani Suna Face Sunnah' Sannan se ya karanto Fadin Allah (s.w.a) cewa:

"Kuma Hakika wannan ne Hanya ta madai-dai ci Sai Ku bi shi (hanyar ta sa), Kuma Kada Kubi wasu hanyo sai su rarrabu daku Ga barin Hanya ta"
[Sutul An'am aya ta 153],

[إمام الشاطبي ya fada a cikin الأعتصام 1/79],

Ibnul Qayyum Yake fada a cikin [ مدارج السالكين 3 /179] cewa an tambayi wani daga cikin A imma game da sunnah sai yace:

"ماﻻ إسم له سوي السنة"
Ma'ana:
"Basu da wani Suna Face sunnah"

Allahu Akbar shi yasa ba'a kiran mu da yan darikar wane... Se dai ajingina mu ga sunnar Annabi (s.a.w) Duk abinda za'a Kira mu dashi zaka ga yana komawa ne Izuwa ga Sunna, To Indai haka ne an raba kenan ku kun dauki naku muma mun dauki namu Shi ya sa idan kace dani:

AHLUSSUNNAH: Daman ni mabiyin Sunnar Annabi ne don haka kowa yana jingina kanshi da shehin sa don ya nuna wanda yake bi ni kuwa se ka jingina ni ga Lamba daya daman kuma ni shi nake bi shine nawa ganin,

In Ka Kirani da:

DAN IZALA: Se nai godewa Allah ka jingina ni ga Kungiyar dake Kauda Bidi'a Tana Tsaida Sunnah, Kungiyar dake Yada Addinin Allah Kaf Africa ynz ma duk duniya Izala ta ratsa, kuma daman ni Dan Izalar ne, Don Haka sai Hamdala,

In ka kirani:

DAN SALAFIYYA: Nan ma dai Kaya ya tsinke a gindin kaba ka siffantani da mai bin Tafakin magabata wanda mun kawo bayani a baya, Kuma dama ai tafarkin su shine abin bi,

In ka kirani:

BAWAHABIYE: Al'wahab Sunan Allah ne Kuma Ni bawan sane!

Allahu Akbar! Sunnah Hantsi Leka Gidan Kowa!!

Zan Tsaya Anan kuma nan ne karshen Yar shimfidar tawa kai tsaye kuma zan kutsa, se a rubutu na gaba,

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah),
29/04/2015,


*Koma Saman Shafi*

→Labarai

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)
.
Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi,
.
Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa,
.
Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunaninsa wai yafi Qaribu Ilmi shine yasa ya dade yana zagin Halifa karibu yana cutar da shi ta ko'ina yana nuna hassadarsa gare shi, dayake dama hassada ga mai rabo taki ce, shi kuma halifa Qaribu kullum sai kara gaba yakeyi har wasu kashashen ma suna bashi lambar yabo ta girmamawa amman duk da haka har yanzu Abdun jabberun yaki ya gane,
.
Ku duba Ko A haife qaribu ya haifi Audujanbiri amman saboda tantiranci da rashin tarbiya babu irin zagin da bayayi masa akwai Lokacin Audu janbiri yace,"qaribu wai babarsa da cikinsa ta shigo gidan malam wai qaribu ba dan malam bane wai shege ne kuma a duba dashi qaribun dashi Audu janbirin waye yake kama da malam kabara, kuma wai a cikin taron daruruwan mutane yayi wannan maganar, ba wannan kadai ba da dai sauran maganganu masu muni wanda shi kuma qaribun dayake yasan kanin nasa yana da ragaggen hankali baya biye ta tashi kullum hakuri yake dashi, lokacin da magoya bayan qaribu suka ga abin nasa fa ya wuce tunani ya koma tsantsar iskanci da rashin mutunci sai sukace suma dai dai suke da dan iska, inda duk lokacin da yazo wani taro ko maukibi sai suki su barshi ya shiga idan ma ya shigo sai su jefe shaidani, haka suka dinga yiwa dan banza daga karshe dayaga uwar bari da kansa yaje ya bawa halifa Qaribu hakuri akayi salhu tun daga lokacin abu ya danyi shiru,
.
Sai yanzu ya tsiro da wani iskancin, yana zagin Halifa qaribullah, dama tun asali kasancewarsa mutum mai neman Suna kota halin qaqa, amman hakan yaki samuwa yasa yake cin zarafi da cin mutuncin mutane sai kaji shi yana zagin babban malami wanda ya haife ya haife shi,
.
haka ya koma ta6o 'yan siyasa wanda duk gomnatin da take kai to sai yayi ta zaginta kenan har sai an bashi wani abun, misali lokacin mulkin kwankwaso na farko haka ya dinga bi yana zagin kwankwaso har sai da kwankwaso ya bashi fili a gwale filin mushe, wanda yanzu haka a cikin filin yayi gidansa yayi masallacin juma'a filin ma hakkin mutane, lokacin da kwankwaso ya tafi shekarau yazo sai ya koma 6angaren shekarau yana masa jagaliya da yaga shekarau baya bukatar tafiya da 'yan jagaliya irinsu sai ya dinga zagin shekarau har yake cewa idan yabi shekarau to shi dan zina ne, ana nan sai malam shekarau yayi masa wani babban Alkhairi wanda ya fito yace duk duniya ibrahim masu girma guda uku ne, da Annabi ibrahim da ibrahim inyass da ibrahim shekarau, lokacin da kwankwaso ya dawo be tafi dashi ba sai ya koma zagin kwankwaso ko lokacin da kwankwaso ya ta6a Annabi S.A.W sai ya dinga zagin kwankwaso har yace dashi ya zama kafiri, haka ya tara mutanensa har ya dauki sulke da kwalkwali ya saka a jikinsa , ya umarci 'yan jagaliyar yaransa suka rike makamai suka fito gari suna zanga zanga, amman yadda zakasan munafiki ne sai gashi lokacin da yake wa 'yan tijjaniya raddi yana siffanta Muhammadu Rabi'u kwankwaso da mai kishin musulunci,
.
Ba 'yan siyasa kadai ba, tuntuni shine yau ya ta6o 'yan izala gobe kaji ya ta6o 'yan tijjaniyya jibi ya ta6o 'yan qadiriya ko wani malami wanda bashi da dariqa, tun mutane suna biye masa har suka gane manufarsa suka gane cewa yana fama da ta6in hankali ta yaya zasu tsaya suna rigima da mahaukaci sai duk suka kyale karen yaje yayi ta haushinsa shi kadai, daya ga haka sai ya canza dabara akan ya samu masoya wanda zai dinga damfararsu 'yan kudaden su, haka yayi ya dinga tara karatu da sunan kishin Annabi da soyayyarsa nan ko babu abinda yake koyawa sai jahilci da dure duren ashariya, Kunji AMIRUL FASIKINA HUJJATUL JAHILINA kenan,
.
Koda matasan suka fuskanci babu wata tsiya na karatu da ake karuwa da Abdun jabberun sai duk suka dinga watsewa suna karewa kamar hatsin guziri, daya fuskanci neman Sunan dayake har yanzu a kano ba'asan da wani Abdun jabberun ba, wanda ko a gwale filin mushe babu wanda yasan dashi, kuma gashi na cefane yana gagararsa sai ya tsiro da wani iskanci da zindikanci na zagin sahabban Annabi inda yaje ya kar6o kwangilar kudi wajen Iro jakin zariya L.A don ya samu magoya baya, lokacin daya fara zagin sahabbai irinsu sayyadi Mu'awiya A,S yana kawo hadisai ta karfin tuwo yana juya musu ma'ana malaman Sunnah sun zabura suna mayar masa da raddi wanda shi dama abinda yake so kenan ayi ta zancensa yayi suna a san dashi, bayan lokacin da malam Alqasim yayi buji buji dashi akan littafinsa muqaddimatul Khaziba, haka aka dinga fama dashi akan yazo a zauna ayi muqabala akan wannan mas'alar ta fi'atul bagiya, amman hakan yaki yuyuwa kullum ya zauna sai dai dure duren ashariya da tsine tsine da karya da cika baki da alfhari da ihu da kowayee, a haka yanzu zindiqancin nasa da iskancin nasa har yazo ya fara zaginsu sayyadi Abubakar yana karyatashi akan hadisin gadon Annabi, yana zagin sayyadi usman akan wai azzalumi ne a lokacin mulkinsa, yanzu da malaman Sunna suka gane cewar bamagujen dan shi'ar yanada ta6in hankali sai duk suka kyale shi, don idan banda me ta6in hankali babu wanda zai dinga zagin sahabbai yana tuhumarsu,
.
To sai rannan mai tatsinen a wani shirmen sa dayake yi wai da sunan karatu yana karanto wani soki burutsun littafinsa mai suna MUQADDIMATUL KHAZIBAH babi mai taken LA TASABBU AS'HABI sai yazo maganar akan wani Hadisi da Halifa Qaribullah ya rawaito akan Sayyadi Ali inda ya dinga ciwa halifa Qaribullah mutunci yana fada masa maganganu na 6atanci yana cewa zasu 6ata dashi akan imami, ba don komai yake haka ba wai don kawai halifa shi yana girmama sahabban Annabi baya zaginsu sannan yana fadar gaskiya a duk inda ta dace, ko a wani haukan karatun Amirul jahilina na baya naji wai har yana cewa wai qaribu yayi maja da 'yan izala yana kiransa da nasibi,
.
To janbiri idan ma izalar qaribu ya koma ai ya gano itace gaskiya ne, tunda gaskiya yake bi, kuma kowa yayi shaidar cewa qaribu malami ne me koyar da karatu wanda yakanyi tafsiri a gidan sarki, sannan a ranaku yakan karanta sahih muslim da Algunya da ishreniyya, ba kamar ka ba wanda babu abinda ka iya sai dai ka tara mutane kayi ta dura ashariya kana tsine tsine kana sheka karya kana hauka suna ihu kana koya musu ta'addanci kana cewa su dauki makamai suje masallacin da akai rikici a baya su kashe 'yan izala, kai saboda ci da qarfi irin na mai mai tatsine sai kaje ka rubuto hadisai da ayoyi kazo kayi ta karantasu da kyar kana kuskure a cikin ayoyin, mutumin da ko haddar simini daya bashi da ita a Qur'ani, kai ko Ayar Muhammadur rasulillah ma daya karanto akwai kusa kurai a cikinta, kai Abduljbbar wallahi jahili ne na karshe, na tabbata ko fatiha ma idan zai karanta sai an ci gyaransa, ayar suratul ma'ida IN TU AZZIBHUM FA INNAHUM IBADUK WA IN TAGFIR LAHUM FA INNAKA ANTAL AZIZUL HAKIM duk da rubuto ayar yayi amman shi jahilin sai cewa yayi FA INNAKA ANTAL GAFURUR RAHIM haka farkon raddinsa ga 'yan tijjaniya yace" ALLAZINA HUM IZA ASABATHUM sai ya sake cewa" ALLAZINA IZA ASABSATUM.. Kunji chakwakiya fa, haka a wani karatunsa yana karanta tarihin matan Annabi S.A.W wai ayar da take suratul Ahzab tana gargadi ga Matan Annabi itace" INKUNTUNNA TURIDNAL HAYATUD DUNYA WAZINATAHA FATA A LAINA UMATTI U KUNNA WA USARRIH KUNNA amman jahilin wai sai yace." FATA A LAINI UDALLIQUKUNNA WA USARRIH KUNNA, kuji jahili wanda beyi karatun Qur'ani ba, sannan ayar ta suratu Ahbaz yazo kan kissar Zainab da zaid ayar itace WAMA KANA LI MU'UMINUN WALA MU'UMINATUN IZA QADALLAHU WARA SULUHU AMRAN AY YAKUNA LAHUMUL KIYARATU MIN AM RIHIM WAYAY YA'ASILLAH WARA SULAHU FAQAD DALLA DALALAN MUBINA amman kasgin jahilin sai yace" FAQAD DALLA DALALAN BA'IDA kunji jahili wanda beyi karatun qur'ani ba. Idan nace zan dinga kawo kuskuren wannan hanfefen sai na kawo sunfi hamsin, don ko aya daya bazai iya ba ammn ya dinga wa Qur'ani Hawan qawara.
.
To wai wannan kuhungun jahilin kasgi, wai a fadar wasu wawayen shine malami kuma wai hanferen shine jagoransu, kai godiya ta tabbata ga Allah daya saka mabiya wannan zindiqin suka kasance wawaye mahaukata, tabbas kamar yadda suke fada na yarda Amirul jahilina shine mujaddadin wawaye na wannan zamani.
.
Abdun jabbarun sai dai kayi hakuri, na gaba yayi gaba na baya sai labari, halifa qaribullah yayi maka nisan da har abada bazaka ta6a kamo koda farcensa saba, sai dai ka cigaba da haukanka da zagin nasa idan bakayi wasa ba hassada itace zata sheke ka har lahira, kuma ko shi Halifa Qaribun yasan kanada matsalar kwakwalwa, wanda ya kamata yasan yadda za'ayi a kaika dawanau tun kafin haukan naka yakai ka fara zagin annabawa kana tuhumarsu, abduljabbar nidai ina maka Addu'ar Allah ya baka lafiya ya rabaka da wannan cutar ta ta6in hankali da take damunka, su kuma jahilan da suke biye maka. Allah ya ganar dasu su fara zuwa makaranta suy karatu, don babu wani mai ilmi da hankalin da zai dauki wannan galmashoran mai dure duren ashariya da zagin sahabban Annabi wai da sunan malami.
.
Tofah dama ance duk yadda akai da jaki dai yaci kara, yanzu gaskiyar nan dana fada fa sai ka samu wasu jakunan sun fara tunkuyi koh? To jakunan kogo ayi ta tunkuyi lafiya, nidai babu jakin daya isa ya tunkuye ni na juya nace zan rama, ko shi kansa babban jakin naku na kogo be isa balle wasu karnukan farauta, saboda haka 'ya'yan mutu'a. Karnukan farauta haihuwar mutu'a kuy ta haushi lafiya.
.
Har yau dai
.
Angom Fatima ne Abban Sadiq
.
I.A.I

Back to posts
Comments:
[2016-02-24 21:46:57] Moh'd B. Ussaini :

To Maza Kaje Ka Tuba Domin Kayi Karya Gami Da Hahilci Bataimiye

[2016-07-01 22:33:04] ANAS AMEEN :

ALLAH YA SAWAKE AMEEN.

[2016-05-12 19:18:42] ummu aisha :

SLM

[2016-07-24 20:41:23] Aminu Rabiu Garun Gudinya Babura :

Ya Allah kaganar damu gaskiya katseratar da diga diganmu daga saba maka amin

[2016-07-30 18:45:55] MHD SANI :

Allah yasaka wa abduljabbar anyi masa kage kuma baze yafeba

[2016-09-17 05:21:32] ibrahimaliyusumaila@gmail.com :

kai arasa wanda za aiwa sharri sai abduljabbar

[2016-08-28 22:57:17] Shamsuddeen lawal anchau :

Tofa!

[2018-02-07 15:24:04] Zaharaddeen m.abubakar deen :

to allah yaimana jagora amin mudai sunnah sak.


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake

Adadin Maziyarta 293022

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358