XtGem Forum catalog
Google69490f6862051cb8
google-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlgoogle-site-verification: google69490f6862051cb8.htmlBasheer journalist sharfadi14

Basheer journalist sharfadi14.jpg6
Basheer journalist sharfadi 11 1
Maraba Da Zuwa Wannan
Shafi Mai Al-barka 1

☀ Zabi inda kake son shiga ☀
Menunks
→Home
→Akidojin Ahlussunnah
→Addinin musulunci (35)
→40 Hadith (50)
→Fadakarwa (120)
→Neman labarai (20)
→Shi'a Kafirci (50)
→Hadith (55)
→Khudubobi (24)
→Tarihin magabata (60)
→Raddi / Maida martani (99)
→Face book post (30)
→Monthly Archives (60)
→Tambaya da Amsa (20)
→Sahabban Annabi {s.aw} (50)
→Taskar maluman sunnah (25)
→Akidar Y'an Shi'a Dangane da Al'kur'ani
→Fassarar Usulussunnah (20)
→Sheik Ja'afar {Rahimahullah} (65)
→Sheik Abubakar Gumi {Rahimahullah} (30)
→Sheik Dr. Muhammad Sani R/Lemo
→Salafiyyah Network Nigeria (100)
→Adam Sani Abu-Umayrah (99)
→Salaf Ustaz (79)
→Malama Ummi Ahmad Katsina
→Malama Amina Saleh Mande
→Labarai (40)
→Nishadantarwa (10)
→Siyasar Nigeria (9)
→Vidio (33)
→Audio (66)
→Hotuna (120)
→Internet Cheat (90)
→Site Achieve
→Application (10)
→Games (8)
→About me (01)

Wannan shafin mallakarCoollogo com-1281358 3
Ne




SHAFI DON KARUWAR MUSULMI
Wannan 6angare InshaAllahu ze dinga zuwa muku ne daga y'ar uwar ku,
Malama Ummi Ahmad Katsina
Kuna Iya Binta ta shafin Face book
Wanda ya tsara kuma ya shirya,
Basheer Journalist Sharfadi


TARBIYYA VOL 1.
.
Tarbiyya -Itace halayya ko dabi'un masu kyau da kowace kowace kabila da jinsi take da nata tsarin.
.
Tarbiyya takunshi abubuwa daban daban Misali mu muslmai kuma hausawa tsarinmu zan iya cewa shine babban tsari.
.
Idan kuka duba duk yaron bahaushe da zai taso cikin tarbiyya mai kyau zakusame shi,abin sha'awa ga kowa.
.
Anan zandakata sai Allah yasake sadamu .



TARBIYYA VOL 2.
.
TAYA ZAMU TARBIYYANTAR DA YARANMU?
.
Icce tun yana danye ake tankwasashi.Dazarar yaronka ya fara gane abu (misali yanada sheka ra biyu) in kinwa taro tsawa kikan firgita shi Ku ma dazarar ya firgita zakiga ya daina abinda a
binda yakeyi. To yana kara girma da wayo kiriniya tana karuwa,dan haka yar'uwa sai kinyi aiki sa nutsuwa,da kulawa sosai akan yaranki.a
.
anan zandakata sai Allah yasake hadamu.



TARBIYYA VOL 3.
.
BA'A TARBIYYA DA DUKA!
.
Idan yaronki yayi maki laifi,kirashi kizaunar dashi agabanki. Kice yanzu Muhammad abi nda kayi ka kyauta kenan?
.
kanaso muyi fushi dakai?
.
Allah baya son abu kaza da kaza da kakeyi.
.
Kina masa nasiha kina gaya masa illolin abin tare da tsoratar dashi. misali,
.
Inka yi kaza Allah zai soka kuma zaibaka lada.
.
Yasaka a aljanna,kaza da kakeyi Allah baya so kuma zaiyi fushi da kai,kadainayi Kaji muhammad a karshe kace Allah yayi maka Albarka,
.
Duk lokacinda yaronka ya bata maki rai kiyi hakuri kada kibishi da muna nan kalamai ko duka,duka bazai kareki da komaiba sai ka rin bacin rai.
.
Anan zandakata Sai Allah ya hada mu a shiri nagaba.



Ummi Ahmad wrote a new note: TARBIYYA VOL 4.
.
SALLAMA.
.
Ki koyawa yaranki SALLAMA kodaga daki suka fito zuwa falo inbasuyi sallama ba ki ce meyasa suka shigo basu yi sallama ba?
.
kice sukoma suyi sallama.Da haka zakiga ya zame masu jiki sun saba,
.
Duk inda suka je sai sunyi sallama zasu shiga.
.
zakiga duk gidan da yaranki suka je ana yabawa tarbiy yanki.
.
Anan zamu kwana muna rakon Allah yabamu ikon tarbiyyantar da yaranmu.



MUKYAUTATA IBADUNMU.
.
Kamar koda yaushe shirin yana kara tunatar damu a kan yanda zamu gyara ibadunmu ta
kowane bangare,Annabi (s.a.w) yace, inayi maku wasiyya da kuyi riko da abu ukku
.
Nafarko sallar wutiri kafin kwanciya bacci
.
Nabiyu yin sallar walha akowace ranan.
.
Na ukku yin azumi 3 acikin wata daya wato
13-14-15.
.
Ya Allah kabamu ikon aikata wan nan wasiyyoyin manzon Allah (s.a.w.) .Ummi
Ahmad.



**KIS-SOSHIN ANNABAWA Kashi na 01**

Assalamu Alaikum InshaAllah ayau zan fara gabatar da shiri na mai suna a sama In da yau. Zamu fara da kissar Annabi Adam (As) kamar yadda muka riga muka sani ne cewa a cikin Alkur'ani mai girma cikin surori daban daban wadanda sukayi magana a kan ainihin yadda ubangiji Allah subhanahu wata'ala ya mana ta yadda ya halicci Annabi Adam (AS).

Allah (SWA) ya halicci Annabi Adam(AS) daga wani jinsi Wanda mu yan Adam muke Rayuwa akanta (wato kasa),Wanda akanta muke Rayuwa kuma a cikinta za'a binne mu, kuma a kanta za'a tashe mu.

Kamar yadda yazo a cikin Alkur'ani mai girma, inda Allah (SWA) yake cewa kamar haka-

"Hakika mune muka Halicci mutum daga kekasasshen Dallakin yumbu Abin Cudanyawa".

Ance yayin da Allah (SWT) yayi nufin zai halicci Annabi Adam (AS)Allah ya yiwa kasa wahayi da cewa hakika nizan halicci wata halitta daga yumbun ki, daga cikin wannan halitta akwai Wanda zai bini sannan kuma daga cikinsu akwai wanda zai saba Mani, wanda ya bini zan shigar dashi Aljannah, Wanda kuma ya saba mani zan shigar dashi wuta.

Anan zandakata sai wani lokaci zanci gaba in shaa Allah.



**KISSOSHIN ANNABAWA Kashi 02**

Ayau inshaa Allah zanci gaba daga inda muka kwana,

Sannan sai Allah s.w.t. ya umarci mala'ika jibrilu A.s. daya sauka izuwa kasa, domin ya damki wani sashi na kasa, to a lokacin da mala'ika jibrilu A.s. ya sauko gareta, domain dibar wannan kasa sai kuwa wannan kasa ta fara yi masa magiya da Allah s.w.a. tana mai cewa, hakika ni ina neman tsari da buwayar ubangijin nan da ya aiko ka, akan kada ka debi komai daga gareni, Wanda har ya kasance daga karshe zai zama wani rabo a cikin wuta, jin wannan magiya da mala'ika jibrilu A.s. yayi sai ya kyaleta ya fasa damkar komai daga gareta. Anan zandakata sai wani makon in shaa Allah daga yar'uwarku Hafsat Ahmad Ummi.



KISSOSHIN ANNABAWA
VOL 3 NA IBN ADAM FAGGE.

Har yanzu muna cikin kissar Annabi Adam.mun tsaya inda mala'ika jibril A.s. yakoma zuwa ga Ubangiji s.w.a yace ya Ubangiji hakika wannan kasa tayi mani magiya da cewa kada in debeta, nikuma sai na kasa diban wani abu daga gareta, to sai ubangiji s.w.a. ya kuma umartar mala'ika mika'ilu A.s. akan cewa yaje domin ya damko wani sashi daga gareta,

Yana zuwa sai shima ta fara yi masa magiya da Allah, irin wadda tayi wa mala'ika jibrilu A.s. sai shima yafasa diban komai daga gareta ya koma ya zuwa ga ubangiji s.w.a. ya gaya masa irin magiyar da tayi wa mala'ika jibrilu A.s. sai ubangiji ya kuma umartar mala'ikan mutuwa da yaje ya damko wani sashi daga gareta, sai ya sauko ya zuwa gareta, kafin ta yi masa magiya sai kawai yasa wani mashi ya caketa dashi, jin wannan cakar da yayi mata sai datayi wata irin girgiza sannan ya mika hannu domin ya daibi wani abu daga gareta, ganin haka da tayi sai shima ta fara yi masa magiya irin wadda tayiwa yan'uwansa, sai ya ce mata ai bin umarnin ubangijina yafi magiyar da zaki yi min, sai kawai yasa hannu ya damko daga gareta, har damka(4).

Anan zandakata daga yar'uwarku Hafsat Ahmad Ummi.



KISSOSHIN ANNABAWA
VOL 4 LITTAFIN IBN ADAM FAGGE.

Haryanzu dai muna cikin kissar Annabi Adam A.S.Munkwana a inda mala'ikan mutuwa ya damko kasa ×4 a damkar farko ya damka ta farko ya damki bakar kasa, adamka ta biyu ya damki farar kasa, a damka ta uku ya damki jar kasa mai taushi da duwatsu,

Madaukakanta da makaskantanta, sannan sai yatafi da ita izuwa ga ubangiji s.w.t.
To yana zuwa da ita sai ubangiji s w.t yace dashi, meyasa dakaje zaka damkota tayi maka magiya ba ka kyale ta ba? Sai mala'ikan mutuwa yace masa, ya Ubangiji ai umarninka yafi, sai Allah s.w.t yace dashi daga yanzu Kaine mala'ikan mutuwa mai karban rayukan bayi, to ance wannan wuri da mala'ikan mutuwa ya damka, sai yakama kuka, sai Allah s.w.t yayi mata wahayi da cewa, da sannu za'a komo miki da abinda a ka damko daga gareki, wannan shine fadin Ubangiji s.w.a kamar yanda yazo cikin Alkur'ani mai girma

"DAGA KASA MUKA HALICCEKU, A KUMA CIKINTA ZAMU MAI DAKU, DAGA CIKINTA NE ZAMU FITO DAKU A WANI ZAMANI NA DABAN".

Sannan sai Allah s.w.a ya umarci mala'ikan mutuwa daya ajiye wannan kasar da ya damko a bakin Kofar gidan aljannah, a lokacin daya ajiye ta, sai kuma Allah s.w.t ya umarci mala'ika Ridwanu wato mai tsaron gidan Aljannah, daya dauki wannan kasa ya kwaba ta da ruwan tasnimu.

Anan zandakata sai Allah s w.t yasake hadamu.


KISSOSHIN ANNABAWA Kashi na 5 Daga Littafin IBN ADAM FaGGE,

Haryanzu muna cikin kissar Annabi Adam.
Ubangiji s.w.t. ya kuma umartar mala'ika jibril A.s. daya koma ya kuma debo wata farar kasa, wadda itace zuciyar kasa gaba daya, ance da wannan kasarce aka halicci Annabawa, to sannan sai aka kwaba wannan kasa da ruwa, har sai da wannan kasa ta zama kwababben yumbu mai daraja to sannan bayan an kwaba sai aka barta har sai da takai tsawon shekara 40, sannan ta zamo dallakin yumbu mai danko danko, sannan aka sake barinta ta kuma kaiwa tsawon shekara 40, a nan ma sai da ta zama kekasasshen yumbu mai amo kamar kasko, to a sannan ne aka suranta gangar jikim Dan Adam dashi wannan kwababben yumbun, aka kwantar dashi akan hanyar da mala'iku suke sauko wa, shima aka barshi anan har tsawon shekara 40, batare da an busa masa rai ba.

Kamar yadda Allah s.w.t. ya bayyana mana a cikin Aqur'ani mai girma, kamar haka:-

''LALLAI TSAWON ZAMANI YA ZOWA MUTUM ALHALIN BAI KASANCE KOMAI ABIN TUNAWA BA''

Ance wannan tsawon zamani da ake nufi shine shekara 40, Annabi Adam A.S. yana kwance ba'a waiga izuwa gareshi ba.

Ance bayan Allah s.w.t. yasa ankwaba wannan yumbu na halittar Annabi Adam A.s. sai aka hada wani girgije aka yiwa wannan yumbun ruwan bakin ciki dana bacin rai, har tsawon shekara 40 sannan kuma akayi masa ruwan farin ciki da nishadi na tsawon shekara 1 tak, saboda haka sai bakin ciki dan Adam yafi farin cikinsa yawa, sannan kuma bacin ransa yafi nishadinsa yawa. Baya ga wannan sai Allah s.w.t. ya bayyanar wa da Annabi Adam AS. Jijiyoyin dari ukku da sittin 360. Sannan kuma ya halittar masa gabobi guda 40. Kuma yayi masa mahadar gwiwa guda 12, a cikin kansa kuma yasa masa wasu kofofi 7 sune kamar haka, kunnuwa 2 idanuwa 2 hanci 2 dakuma sannan ya sanya masa hannaye da kafafuwa, da sauran abubuwa ya kuma kammala halittarsa cikakkiyar halitta,

Madalla da ubangiji Wanda yafi kowa iya halitta.anan zamu kwana sai Allah yasake sadamu.

Ummi Ahamd,




Koma saman shafi

→Labarai

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)

HASSADA MUGUN CIWO, ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA,(Imam Aliyu Indabawa)
.
Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi,
.
Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa,
.
Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunaninsa wai yafi Qaribu Ilmi shine yasa ya dade yana zagin Halifa karibu yana cutar da shi ta ko'ina yana nuna hassadarsa gare shi, dayake dama hassada ga mai rabo taki ce, shi kuma halifa Qaribu kullum sai kara gaba yakeyi har wasu kashashen ma suna bashi lambar yabo ta girmamawa amman duk da haka har yanzu Abdun jabberun yaki ya gane,
.
Ku duba Ko A haife qaribu ya haifi Audujanbiri amman saboda tantiranci da rashin tarbiya babu irin zagin da bayayi masa akwai Lokacin Audu janbiri yace,"qaribu wai babarsa da cikinsa ta shigo gidan malam wai qaribu ba dan malam bane wai shege ne kuma a duba dashi qaribun dashi Audu janbirin waye yake kama da malam kabara, kuma wai a cikin taron daruruwan mutane yayi wannan maganar, ba wannan kadai ba da dai sauran maganganu masu muni wanda shi kuma qaribun dayake yasan kanin nasa yana da ragaggen hankali baya biye ta tashi kullum hakuri yake dashi, lokacin da magoya bayan qaribu suka ga abin nasa fa ya wuce tunani ya koma tsantsar iskanci da rashin mutunci sai sukace suma dai dai suke da dan iska, inda duk lokacin da yazo wani taro ko maukibi sai suki su barshi ya shiga idan ma ya shigo sai su jefe shaidani, haka suka dinga yiwa dan banza daga karshe dayaga uwar bari da kansa yaje ya bawa halifa Qaribu hakuri akayi salhu tun daga lokacin abu ya danyi shiru,
.
Sai yanzu ya tsiro da wani iskancin, yana zagin Halifa qaribullah, dama tun asali kasancewarsa mutum mai neman Suna kota halin qaqa, amman hakan yaki samuwa yasa yake cin zarafi da cin mutuncin mutane sai kaji shi yana zagin babban malami wanda ya haife ya haife shi,
.
haka ya koma ta6o 'yan siyasa wanda duk gomnatin da take kai to sai yayi ta zaginta kenan har sai an bashi wani abun, misali lokacin mulkin kwankwaso na farko haka ya dinga bi yana zagin kwankwaso har sai da kwankwaso ya bashi fili a gwale filin mushe, wanda yanzu haka a cikin filin yayi gidansa yayi masallacin juma'a filin ma hakkin mutane, lokacin da kwankwaso ya tafi shekarau yazo sai ya koma 6angaren shekarau yana masa jagaliya da yaga shekarau baya bukatar tafiya da 'yan jagaliya irinsu sai ya dinga zagin shekarau har yake cewa idan yabi shekarau to shi dan zina ne, ana nan sai malam shekarau yayi masa wani babban Alkhairi wanda ya fito yace duk duniya ibrahim masu girma guda uku ne, da Annabi ibrahim da ibrahim inyass da ibrahim shekarau, lokacin da kwankwaso ya dawo be tafi dashi ba sai ya koma zagin kwankwaso ko lokacin da kwankwaso ya ta6a Annabi S.A.W sai ya dinga zagin kwankwaso har yace dashi ya zama kafiri, haka ya tara mutanensa har ya dauki sulke da kwalkwali ya saka a jikinsa , ya umarci 'yan jagaliyar yaransa suka rike makamai suka fito gari suna zanga zanga, amman yadda zakasan munafiki ne sai gashi lokacin da yake wa 'yan tijjaniya raddi yana siffanta Muhammadu Rabi'u kwankwaso da mai kishin musulunci,
.
Ba 'yan siyasa kadai ba, tuntuni shine yau ya ta6o 'yan izala gobe kaji ya ta6o 'yan tijjaniyya jibi ya ta6o 'yan qadiriya ko wani malami wanda bashi da dariqa, tun mutane suna biye masa har suka gane manufarsa suka gane cewa yana fama da ta6in hankali ta yaya zasu tsaya suna rigima da mahaukaci sai duk suka kyale karen yaje yayi ta haushinsa shi kadai, daya ga haka sai ya canza dabara akan ya samu masoya wanda zai dinga damfararsu 'yan kudaden su, haka yayi ya dinga tara karatu da sunan kishin Annabi da soyayyarsa nan ko babu abinda yake koyawa sai jahilci da dure duren ashariya, Kunji AMIRUL FASIKINA HUJJATUL JAHILINA kenan,
.
Koda matasan suka fuskanci babu wata tsiya na karatu da ake karuwa da Abdun jabberun sai duk suka dinga watsewa suna karewa kamar hatsin guziri, daya fuskanci neman Sunan dayake har yanzu a kano ba'asan da wani Abdun jabberun ba, wanda ko a gwale filin mushe babu wanda yasan dashi, kuma gashi na cefane yana gagararsa sai ya tsiro da wani iskanci da zindikanci na zagin sahabban Annabi inda yaje ya kar6o kwangilar kudi wajen Iro jakin zariya L.A don ya samu magoya baya, lokacin daya fara zagin sahabbai irinsu sayyadi Mu'awiya A,S yana kawo hadisai ta karfin tuwo yana juya musu ma'ana malaman Sunnah sun zabura suna mayar masa da raddi wanda shi dama abinda yake so kenan ayi ta zancensa yayi suna a san dashi, bayan lokacin da malam Alqasim yayi buji buji dashi akan littafinsa muqaddimatul Khaziba, haka aka dinga fama dashi akan yazo a zauna ayi muqabala akan wannan mas'alar ta fi'atul bagiya, amman hakan yaki yuyuwa kullum ya zauna sai dai dure duren ashariya da tsine tsine da karya da cika baki da alfhari da ihu da kowayee, a haka yanzu zindiqancin nasa da iskancin nasa har yazo ya fara zaginsu sayyadi Abubakar yana karyatashi akan hadisin gadon Annabi, yana zagin sayyadi usman akan wai azzalumi ne a lokacin mulkinsa, yanzu da malaman Sunna suka gane cewar bamagujen dan shi'ar yanada ta6in hankali sai duk suka kyale shi, don idan banda me ta6in hankali babu wanda zai dinga zagin sahabbai yana tuhumarsu,
.
To sai rannan mai tatsinen a wani shirmen sa dayake yi wai da sunan karatu yana karanto wani soki burutsun littafinsa mai suna MUQADDIMATUL KHAZIBAH babi mai taken LA TASABBU AS'HABI sai yazo maganar akan wani Hadisi da Halifa Qaribullah ya rawaito akan Sayyadi Ali inda ya dinga ciwa halifa Qaribullah mutunci yana fada masa maganganu na 6atanci yana cewa zasu 6ata dashi akan imami, ba don komai yake haka ba wai don kawai halifa shi yana girmama sahabban Annabi baya zaginsu sannan yana fadar gaskiya a duk inda ta dace, ko a wani haukan karatun Amirul jahilina na baya naji wai har yana cewa wai qaribu yayi maja da 'yan izala yana kiransa da nasibi,
.
To janbiri idan ma izalar qaribu ya koma ai ya gano itace gaskiya ne, tunda gaskiya yake bi, kuma kowa yayi shaidar cewa qaribu malami ne me koyar da karatu wanda yakanyi tafsiri a gidan sarki, sannan a ranaku yakan karanta sahih muslim da Algunya da ishreniyya, ba kamar ka ba wanda babu abinda ka iya sai dai ka tara mutane kayi ta dura ashariya kana tsine tsine kana sheka karya kana hauka suna ihu kana koya musu ta'addanci kana cewa su dauki makamai suje masallacin da akai rikici a baya su kashe 'yan izala, kai saboda ci da qarfi irin na mai mai tatsine sai kaje ka rubuto hadisai da ayoyi kazo kayi ta karantasu da kyar kana kuskure a cikin ayoyin, mutumin da ko haddar simini daya bashi da ita a Qur'ani, kai ko Ayar Muhammadur rasulillah ma daya karanto akwai kusa kurai a cikinta, kai Abduljbbar wallahi jahili ne na karshe, na tabbata ko fatiha ma idan zai karanta sai an ci gyaransa, ayar suratul ma'ida IN TU AZZIBHUM FA INNAHUM IBADUK WA IN TAGFIR LAHUM FA INNAKA ANTAL AZIZUL HAKIM duk da rubuto ayar yayi amman shi jahilin sai cewa yayi FA INNAKA ANTAL GAFURUR RAHIM haka farkon raddinsa ga 'yan tijjaniya yace" ALLAZINA HUM IZA ASABATHUM sai ya sake cewa" ALLAZINA IZA ASABSATUM.. Kunji chakwakiya fa, haka a wani karatunsa yana karanta tarihin matan Annabi S.A.W wai ayar da take suratul Ahzab tana gargadi ga Matan Annabi itace" INKUNTUNNA TURIDNAL HAYATUD DUNYA WAZINATAHA FATA A LAINA UMATTI U KUNNA WA USARRIH KUNNA amman jahilin wai sai yace." FATA A LAINI UDALLIQUKUNNA WA USARRIH KUNNA, kuji jahili wanda beyi karatun Qur'ani ba, sannan ayar ta suratu Ahbaz yazo kan kissar Zainab da zaid ayar itace WAMA KANA LI MU'UMINUN WALA MU'UMINATUN IZA QADALLAHU WARA SULUHU AMRAN AY YAKUNA LAHUMUL KIYARATU MIN AM RIHIM WAYAY YA'ASILLAH WARA SULAHU FAQAD DALLA DALALAN MUBINA amman kasgin jahilin sai yace" FAQAD DALLA DALALAN BA'IDA kunji jahili wanda beyi karatun qur'ani ba. Idan nace zan dinga kawo kuskuren wannan hanfefen sai na kawo sunfi hamsin, don ko aya daya bazai iya ba ammn ya dinga wa Qur'ani Hawan qawara.
.
To wai wannan kuhungun jahilin kasgi, wai a fadar wasu wawayen shine malami kuma wai hanferen shine jagoransu, kai godiya ta tabbata ga Allah daya saka mabiya wannan zindiqin suka kasance wawaye mahaukata, tabbas kamar yadda suke fada na yarda Amirul jahilina shine mujaddadin wawaye na wannan zamani.
.
Abdun jabbarun sai dai kayi hakuri, na gaba yayi gaba na baya sai labari, halifa qaribullah yayi maka nisan da har abada bazaka ta6a kamo koda farcensa saba, sai dai ka cigaba da haukanka da zagin nasa idan bakayi wasa ba hassada itace zata sheke ka har lahira, kuma ko shi Halifa Qaribun yasan kanada matsalar kwakwalwa, wanda ya kamata yasan yadda za'ayi a kaika dawanau tun kafin haukan naka yakai ka fara zagin annabawa kana tuhumarsu, abduljabbar nidai ina maka Addu'ar Allah ya baka lafiya ya rabaka da wannan cutar ta ta6in hankali da take damunka, su kuma jahilan da suke biye maka. Allah ya ganar dasu su fara zuwa makaranta suy karatu, don babu wani mai ilmi da hankalin da zai dauki wannan galmashoran mai dure duren ashariya da zagin sahabban Annabi wai da sunan malami.
.
Tofah dama ance duk yadda akai da jaki dai yaci kara, yanzu gaskiyar nan dana fada fa sai ka samu wasu jakunan sun fara tunkuyi koh? To jakunan kogo ayi ta tunkuyi lafiya, nidai babu jakin daya isa ya tunkuye ni na juya nace zan rama, ko shi kansa babban jakin naku na kogo be isa balle wasu karnukan farauta, saboda haka 'ya'yan mutu'a. Karnukan farauta haihuwar mutu'a kuy ta haushi lafiya.
.
Har yau dai
.
Angom Fatima ne Abban Sadiq
.
I.A.I

Back to posts
Comments:
[2016-02-24 21:46:57] Moh'd B. Ussaini :

To Maza Kaje Ka Tuba Domin Kayi Karya Gami Da Hahilci Bataimiye

[2016-07-01 22:33:04] ANAS AMEEN :

ALLAH YA SAWAKE AMEEN.

[2016-05-12 19:18:42] ummu aisha :

SLM

[2016-07-24 20:41:23] Aminu Rabiu Garun Gudinya Babura :

Ya Allah kaganar damu gaskiya katseratar da diga diganmu daga saba maka amin

[2016-07-30 18:45:55] MHD SANI :

Allah yasaka wa abduljabbar anyi masa kage kuma baze yafeba

[2016-09-17 05:21:32] ibrahimaliyusumaila@gmail.com :

kai arasa wanda za aiwa sharri sai abduljabbar

[2016-08-28 22:57:17] Shamsuddeen lawal anchau :

Tofa!

[2018-02-07 15:24:04] Zaharaddeen m.abubakar deen :

to allah yaimana jagora amin mudai sunnah sak.


UNDER MAINTENANCE

Share|

Kaima shiga a tattauna da kai
* No boards.

Online: Guests: 1


→Ra'ayin jama'a game damu

 IDAN KANA BUKATAR A TALLATA MAKA HAJAR KA A WANNAN SHAFIN DA SAURAN SHAFUKAN MU KANA IYA TUNTUBAR MU TA WADANNAN HANYOYIN KAMAR HAKA:


Email: bjournalist55@hotmail.com

Phone No: 09035830253

Facebook: Basheer Journalist Sharfadi

Address: Ittihad Computer Centre,  No 92 Daneji Kano


MAI TALLA SHI KE DA RIBA


*Bayanan ka*
Browser din da ka hawo Mozilla

Kasar da kake

Adadin Maziyarta 242370

Adadin Wadanda Sukayi Comment 65691

A Wadanda Suka Shiga Tattaunawar Mu 54


Follow @bjournalist55
→Yi Adding Dina Ta Facebook
→Yi Like Na Dakarun Sunnah Page
→Yi Like Dina Ta Facebook

*Shafuka Masu Alaka Da Mu*

→Basheer Sharfadi wordpress
Basheer Sharfadi Blog Spot
UP
→Home

Basheer Journalist Sharfadi (Abu Hafsah)
ISLAMIC DATE
  • phpimg2.php?it&ic=yellow



  • Click to Sms
    Click to Call


    Basheer journalist sharfadi3
    Coollogo com-1281358